Zanga-zanga: Yadda harkokin Kasuwanci suka tsaya chak a Nigeria

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Harkokin Kasuwanci sun tsaya chak sakamakon fara zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a manyan birane dake jihohin Nigeria baki daya.

A jihohin Kano, Kaduna Legos Fatakwal da Abuja bankuna da kasuwanci sun kasance a rufe da sanyin safiyar wannan rana ta alhamis saboda zanga-zanga da ake gudanarwa a fadin kasar.

Manya hanyoyi suma sun kasance babu kowa yayin da masu zanga-zangar suka bijirewa kiraye-kirayen da mahukunta suka rika yi na dakatar da zanga-zangar.

Talla
Talla

Titunan da aka saba samun cunkoson jama’a a Kaduna babu kowa, yayin da masu zanga-zangar suka fito kan tituna suna nuna korafe-korafen su game da tsadar rayuwa suke ciki.

Haka a Kano ma Mutane sun fito a manyan titunan jihar sun dauke da kwalaye da ke nuna bukatarsu ta dawo da tallafin man fetur da dawo da darajar naira da kuma magance tsadar kayan abinchi.

Hotunan Yadda Matasa da Dattawa Su ka Fito Zanga-zanga a Kano

An rufe bankuna, kasuwanni, da sauran wuraren kasuwanci a Owerri saboda fitowar masu zanga-zangar kamar yadda gidan talabijin na Channels suka rawaito.

Tsayarwar harkokin Kasuwanci a Manyan biranen Nigeria na nuni da cewa tattalin arzikin Nigeria zai sami nakasu sosai, saboda komai ya tsaya ballantana gwamnati ta sami kudaden shiga.

Waɗannan suka shirya zanga-zangar sun bayyana cewa za su kwashe kimanin Kwanaki 10 suna gudanar da zanga-zangar ta adawa da tsadar rayuwa a Nigeria.

Sai dai rahotannin da jaridar kadaura24 ke samu sun nuna cewa an jibge tarin jami’an tsaro a wurare daban-daban a dukkanin jihohin tarayyar Nigeria, don ganin zanga-zanga ba ta rikide ta koma tashin hankali ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...