Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Makon Lafiyar Mata da Kananan Yara na 2024

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da zagayen farko na makon lafiyar mata, jarirai da kananan yara na shekarar 2024 a hukumance.

Hakan na kunshi ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Juma’a.

A jawabinsa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada cewa makon lafiyar mata da kananan yara na da burin inganta kiwon lafiyarsu ta hanyar mayar da hankali da daukar matakan rigakafi da magance cutar da ke addabar iyaye mata da yara.

Talla
Talla

Ya kara da cewa, taron na tsawon mako guda wata dama ce ga mata da kananan yara domin su kara samun kulawa ta hanyar tsarin kiwon lafiya da ake da su, wanda ke kara karfafa ayyukan kula da lafiyar mata da kananan yara kyauta da ake samu a kanana da manyan asibitocin jihacin da ke jihar.

Gwamna Yusuf ya ce gwamnatin jihar Kano na ci gaba da jajircewa wajen aiwatar da shirye-shiryen kiwon lafiya da nufin inganta rayuwar al’ummarta.

Yanzu-yanzu: Yan sanda sun bayyana sharudda ga masu son shiga zanga-zanga a Nigeria

Ya nanata kudurin gwamnatinsa na rage mace-macen mata da kananan yara da kuma shawo kan cututtukan da za a iya magance su kamar su zazzabin cizon sauro, HIV, da tarin fuka.

Tun da farko kwamishinan lafiya na jihar Dr. Abubakar Labaran Yusuf ya bayyana cewa Manufar makon kula da lafiyar mata da kananan yara shi ne samar da cikakkiyar kulawa ga mata masu juna biyu tun daga daukar ciki har haihuwa da kuma tabbatar da jin dadin jarirai da yara ‘yan kasa da shekaru biyar.

Talla

Dakta Labaran ya bayyana jin dadinsa da yadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jajirce wajen kula da fannin kiwon lafiya tare da bada tabbacin cewa ma’aikatan lafiya a jihar Kano sun kuduri aniyar samar da ayyuka masu inganci ga al’umma.

Taron ya sami halartar wakilin Sarkin Kano, Turakin Kano kuma Hakimin Dala, Alhaji Abdullahi Lamido Sanusi, da wakilan kungiyoyin ba da tallafi a bangaren lafiya da suka hada da NPHCDA, UNICEF, WHO, ALIVE & THRIVE, da MSF.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...