Ni ma na sha yin zanga-zanga amma ta lumana – Bola Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce shi ma ya sha shiga zanga-zanga a lokacin mulkin soja “amma ba tare da tashin hankali ba”.

Shugaban na magana ne yayin da gwamnatinsa ke ta roƙon masu shirya zanga-zanga game da tsadar rayuwa da su ƙara mata lokaci don maganace matsalolinsu cikin ruwan sanyi.

Talla
Talla

“A lokacin mulkin soja, mun yi adawa da ‘yan kama-karya, kuma ina cikin mutanen da suka dinga zanga-zangar lumana ba tare da ƙone-ƙone ba,” a cewar shugaban lokacin da yake karɓar baƙuncin Jakadan Amurka a Najeriya Richard Mills Jr. a yammacin yau.

DSS Ta Ce Ta Gano Manufar Masu Son Yin Zanga-Zanga a Nigeria

Ya ci gaba da cewa “mun yi bakin ƙoƙarinmu wajen tabbatuwar shekara 25 ta mulkin dimokuraɗiyya a jere kuma zan yi cigaba da rainon wannan dimokuraɗiyyar”, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ta bayyana.

 

Hukumar tsaron farin kaya ta ƙasar, DSS, ta yi gargaɗi dangane da shirin zanga-zangar tana mai cewa “burinsu shi ne kifar da gwamnati”.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...