Karin Haske Kan Hukuncin Kotu Game da Rikicin Masarautun Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Babbar Kotun Kano ta umarci sarakunan masarautun jihar da aka tube da su mayar mata da duk wani kaya mallakar gwamnati da ke hannunsu.

Kotun ta tabbatar da nadin Sarki Muhammadu Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 16, ta kuma haramta wa wadanda aka rusa masarautun nasu bayyana kansu a matsayin sarakuna.

Da take yanke hukuncin a ranar Alhamis, Mai sharia Amina Adamu Aliyu ta tabbatar da ikon da majalisar dokokin jihar Kano na yin dokoki.

Talla

Alkalin ta ci gaba da cewa don haka gyaran dokar masaraun jihar da majalisar ta yi yana kan ka’ida, haka ma hannun da Gwamna Abba Kabir ya yi a kan dokar wadda ta nada Sarki Muhammadu Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 16, bai saboda doka ba.

Kotun ta ce ta yanke wannan hukuncin ne bisa dogaro da sashi na 4,5,7, (a da b) sai kuma sashi na 101 a da a na kundin tsarin mulki Nigeria.

Dalilin da ya haifar da ruɗani a majalisar dokokin jihar kano akan Ganduje

Alƙalin ta kara da cewa abun da jami’an tsaro suka yi na dawo da sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero kuma suke gadin shi a gidan sarki na Nasarawa ya sabawa doka.

Sai dai kotun ta ki amincewa da rokon masu kara na cewa a fitar da Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero daga Fadar Nassarawa.

Alkalin ta ce wannan ba hurumin kotun ba ne sai dai su kai wannan bukatar ga kotun tirabunal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...