Dalilin da ya haifar da ruɗani a majalisar dokokin jihar kano akan Ganduje

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Majalisar dokokin jihar Kano ta fada cikin rudani lokacin da kakakin majalisar Jibril Isma’il Falgore ya kirawo tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban riko na jam’iyyar APC na kasa.

kakakin majalisar cewa Ganduje shugaban rikon jam’iyyar APC ne a lokacin da yake mika sakon ta’aziyya ga uwargidansa Farfesa Hafsat Ganduje kan rasuwar mahaifiyarta, wanda ya haifar da zazzafar muhawara.

Shugaban marasa rinjaye na majalisar Labaran Abdul Madari da wasu ‘yan majalisar APC ne suka fito da batun, inda suka ce yanzu Ganduje ne cikakken shugaban jam’iyyar APC na kasa ba shugaban riko ba ne.

Talla

Daga bisani majalisar ta dage zaman har zuwa ranar Talata.

A wannan rana ce dai majalisar dokokin jihar Kanon ta dawo zama tun bayan hutun kwanaki 48 da ta yi, wanda ta tafi bayan zartar da kudirin dokar soke masarautu biyar na jihar Kano.

Samoa: Gwamnatin Tinubu na yunkurin danne hakkin yan jarida – Atiku Abubakar

Rahotanni sun nuna cewa an majalisar ta jinkirta komawa bakin aikinta ne saboda matsalar tsaro da ta taso bayan rushe masarautun.

 

Nigerian Tranker

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...