Yau Katun Ƙoli Za ta Yanke Hukunci Kan Shari’ar Da Tinubu Ya Kai Karar Gwamnonin Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

A yau ne ake sa ran kotun koli za ta yanke hukunci kan karar da gwamnatin tarayya ta shigar a kan gwamnonin jihohi 36, Inda ta ke neman kotun ta tilastawa gwamnonin baiwa kananan hukumomi 774 na kasar nan yancin cin gashin kansu.

Kotun kolin ta sanar da dukkan bangarorin da ke kara ta hannun lauyoyinsu cewa a yau zata yanke hukuncin .

Talla

Kotun kolin dai a ranar 13 ga watan Yuni ta dage yanke hukunci kan karar da ake zargin gwamnatocin jihohi. A zaman da aka yi na karshe, tawagar alƙalai bakwai karkashin jagorancin Mai Shari’a Garba Lawal, ya bayyana cewa a shirye suke da za su yanke hukunci bayan sauraron bahasi daga gwamnonin jihohin kasar nan 36, wadanda manyan lauyoyinsu suka wakilce su.

Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Jihohin dai sun yi zargin cewa Lateef Fagbemi, babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a ba shi da hurumin fara daukar matakin a madadin gwamnatin tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...