Kashim Shettima Ya Gargadi Gwamnan Sakoto Kan Tsige Sarkin Musulmi

Date:

Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya gargadi Gwamnan Jihar Sakkwato kan yunkurinsa na tsige Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.

Shettima ya bayyana cewa darajar kujerar Sarkin Musulmi ta wuce iya Jihar Sakkwato, don haka ba abar was ba ce, kuma wajibi ne a ba shi kowace irin kariya da girmamawa.

Shettima ya bayyana haka ne a yayin da ake rade-radin Gwamnan Sakkwato Ahmad Aliyu na shirin tube rawanin Sarkin Musulmi.

Gwamnan Sakoto Na Shirin Tsige Sarkin Musulmi —MURIC

“Sakona ga Mataimakin Gwamnan Sakkwato (wanda ke wakiltar gwamnansa a nan) mai sauki ne: hakika Sultan na Sakkwato a karkashin Jihar Sakkwato yake, amma tabbas darajarsa ta wuce iya nan.

“Sarkin Musulmi wani bango ne da dukkanmu a wannan kasar ke bukatar mu mutunta tare da ba shi kariya da goyon baya mu kuma adana,” in ji mataimakin shugaban kasar.

’Yan Sanda Sun Kori ’Yan Tauri Daga Fadar Sarkin Kano

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a taron tsaro da zaman lafiya na yankin Arewa maso Yamma a ranar Litinin a Kastina.

Mataimakin Gwamnan Sakkwato ne ya wakilci Gwamna Ahmad Aliyu a taron.

Daily trust ta ruwaito Kungiyar Kare Hakkokin Musulmi (MURIC) ta zargi Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmad Aliyu da yunkurin tsige Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.

Babban-Daraktan MURIC, Farfesa Isiaq Akintola, ya bayyana takaici bisa abin da ya kira shirin gwamnan na fakewa da dalilinsa na tsige wasu sarakunan gargajiya 15 a matsayin hujjar tube Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar.

Sarkin Musulmi shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya da kuma Kungiyar Musulmi ta Jama’atu Nasril Islam (JNI).

A watan Afrilu ne gwamnan ya Aliyu ya tube wasu sarakunan gargajiya 15 kan laifukan da suka danganci rashin tsaro da kuma rikicin filaye a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...