Yanzu-yanzu: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Sarautar Kano

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Babbar kotun tarayya da ke Kano ta yi watsi da duk wani mataki da gwamnatin jihar Kano ta dauka na soke dokar masarautar Kano.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Majalisar dokokin Kano ta soke dokar bayan haka Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aiwatar da ita ta hanyar tsige Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin Sarkin Kano.

Gwamnan ya kuma rushe masarautu hudun da suka hada da Bichi da Rano Karaye da kuma Gaya, wanda tsohon gwamnan jihar kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya samar.

Hadimin gwamnatin Kano ya yiwa Kawu Sumaila, Hanga da yan majalisu 17 wankin Babban Bargo kan rikicin Sarauta Kano

Gwamnan ya dogara da dokar ne wajen sake nada Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II, wanda Ganduje ya tsige a shekarar 2020, a matsayin Sarkin Kano na 16.

Rikicin Sarautar Kano: Yan Sanda sun Gargaɗi Mafarauta yan Banga da sauran jama’a

Sai dai Aminu Babba Danagundi, Sarkin Dawaki Babba, ya kalubalanci tanade-tanaden dokar, ya kuma bukaci kotun ta bakin lauyansa, Chikaosolu Ojukwu (SAN), ta yi watsi da sabuwar dokar.

A hukuncin da ya yanke a ranar Alhamis, mai shari’a Abdullahi Muhammad Liman, ya yi watsi da matakin da gwamnatin Kano ta dauka, inda ya umurci dukkanin bangarorin da abun ya shafa da su ci gaba da kasancewa a matsayin su .

Garin bayani na nan tafe…

 

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...