Bayan janye takunkumin da yan jaridu su ka sawa gwamnatin Kano, sun bayyana dalilan su

Date:

Daga Samira Ahmad

 

Kungiyar wakilan kafafen yada labaran Nigeria dake aikin a Kano ta ce ta janye takunkumin da ta kakabawa gwamnatin jihar Kano saboda masalayar al’ummar jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar Alhaji Aminu Ahmed Garko ya sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24.

Sanarwar ta ce kungiyar ta dauki matakin janye takunkumin ne jim kadan bayan wani taron gaggawar da ta gudanar domin duba batun kauracewa aiyukan gwamnatin Kano har na tsahon kwanaki 14 .

Hotunan Yadda Sarki Sanusi II ya gudanar da Sallar idi a masallacin Juma’a na Kofar Mata dake Kano

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito kungiyar ta ce ta dauki wancan matakin ne domin nuna rashin amincewa da yadda gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ke tafiyar da harkokin gwamnati da kuma yadda take mu’amalantar Manema labarai a jihar.

“Mun fahimci ce ce matakin da muka dauka na kauracewa aiyukan gwamnatin Kano Zai shafi al’ummar jihar musamman a irin wannan lokaci da Ake samun rikicin Sarauta , don haka muna janye takunkumin”. A cewar Garko

Hotunan Yadda Sarki Aminu Ado Bayero ya halarci sallar idi a gidan sarki na Nassarawa a jihar Kano

Kungiyar ta ce yanzu saboda al’ummar jihar Kano zasu cigaba da daukar rahotonnin gwamnatin, amma sun ce za su tabbatar da cewa gwamnatin tana sauke nauyin da al’ummar suka dora mata.

“Mun yaba da fahimta da goyon bayan da jama’a suka ba mu a wannan lokaci, kuma mun yi alkawarin sake sadaukar da kan mu ga aikin da kundin tsarin mulki ya ba mu na fadakarwa da wayar da kan jama’a.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...