Rikicin Sarautar Kano: Kotu ta umarci Gwamnatin Kano ta biya Sarki Aminu Ado Bayero Diyyar Naira miliyan 10

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Babbar Kotun Tarayya mai lamba 3 dake zaman ta a Kano, karkashin jagorancin mai Shari’a Simon Amobeda, ta umarci gwamnatin jihar Kano ta biya Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero diyyar naira Miliyan 10, sakamakon ta ke masa hakki da tsoratar da shi.

Kadaura24 ta rawaito tunda farko dai Lauyan mai kara Barr. Mamman Lawan Yusuf ya shigar da karar ne a madadin Alhaji Aminu Ado Bayero yana rokon Kotu da ta bi masa hakkinsa na Dan’adam da yake zargin an ta ke masa.

A karar da ya shigar Alhaji Aminu Ado Bayero yace umarnin da gwamnan kano ya bayar na sanyan yan sanda su kama shi, ba tare da ya aikata wani laifi ba, inda ya ce hakan ya saba da sashi na 4 na kundin tsarin mulkin Nigeria .

Manoma sun bukaci gwamnan Kano ya cire kwamishinan Noma na jihar

Bayan sauraron rokon, Kotun ta yi hukuncin cewa Gwamnantin jihar Kano ta biya mai karar Naira miliyan 10, sannan yana da damar yin yawo a ko ina a Najeria.

Daga bisani Kotun ta bayyana cewa tana da ikon Sauraran Shari’ar da Sarki na 15 ya shigar

Bayan fito wa daga Kotun Lauyan Aminu Ado, Abdurrazak Ahmad, ya shaida wa jaridar manema labarai cewar kotun ta yadda lallai gwamnatin jahar Kano, ta keta hurimin da dokar kasa ta ba wa sarki na 15, don a kama shi har sai da ingantaccen dalili.

Rikicin Sarautar Kano: Kotu ta yi kwarya-kwaryar hukunci

Kazalika Lauyan Gwamnatin Jahar Kano Barr Ibrahim Isa Wangida ya bayyana cewa, wannan hukuncin da kotun ta yi nasara ce a Gare su , domin ba a taba mutuncin sarkin Kano na 16 Muhammadu Sunusi ii ba, inda ma su karar suka roki kotun ta cire shi daga gidansa amma kotun bata bayar da damar hakan ba.

Ya Kara da cewa za su sanar da wadanda suke wakilta , idan da akwai yiwuwar daukaka kara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...