Tinubu ya mayar da martani game da faduwar da ya yi lokacin hawa mota

Date:

 

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya mayar da martani kan faduwar da ya yi lokacin bikin ranar dimokuraɗiyya ta 12 ga watan Yunin 2024.

Bidiyon faduwar shugaban ya yaɗu a shafukan sada zumunta wanda ya nuna Tinubu a lokacin da yake yunkurin shiga motar faretin a dandalin Eagle Square da ke Abuja inda ya rasa wani mataki wajen hawar motar ya faɗi.

Tinubu mai shekaru 72, ya ce dimokraɗiyya ta cancanci faduwa.

Ranar Dimokaradiyya: Minista Abdullahi Gwarzo ya Bayyana Nasarorin Tinubu

Da yake magana game da abin da ya faru a ranar Laraba, shugaban ya yi dariya da cewa “na rusuna ne don girmama dimokraɗiyya” a salon Yarbawa.

Shugaba Tinubu ya kuma yi amfani da taron liyafar cin abincin na bikin dimokraɗiyya wajen kira ga hadin kan Nijeriya, ba tare da la’akari da kabila ko addini ko siyasa ba.

Tsadar Rayuwa: Kar ku biye wa masu son yin zanga-zanga a Kano – Amb. Ibrahim Waiya

Ya kuma jaddada cewa hadin kan Najeriya ba abu ne da za a iya yin cinikinsa ba.

Bayan afkuwar lamarin, an samu martani da dama daga ‘yan Najeriya daban-daban ciki har da ‘yan adawa.

BBC Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...