Tinubu ya mayar da martani game da faduwar da ya yi lokacin hawa mota

Date:

 

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya mayar da martani kan faduwar da ya yi lokacin bikin ranar dimokuraɗiyya ta 12 ga watan Yunin 2024.

Bidiyon faduwar shugaban ya yaɗu a shafukan sada zumunta wanda ya nuna Tinubu a lokacin da yake yunkurin shiga motar faretin a dandalin Eagle Square da ke Abuja inda ya rasa wani mataki wajen hawar motar ya faɗi.

Tinubu mai shekaru 72, ya ce dimokraɗiyya ta cancanci faduwa.

Ranar Dimokaradiyya: Minista Abdullahi Gwarzo ya Bayyana Nasarorin Tinubu

Da yake magana game da abin da ya faru a ranar Laraba, shugaban ya yi dariya da cewa “na rusuna ne don girmama dimokraɗiyya” a salon Yarbawa.

Shugaba Tinubu ya kuma yi amfani da taron liyafar cin abincin na bikin dimokraɗiyya wajen kira ga hadin kan Nijeriya, ba tare da la’akari da kabila ko addini ko siyasa ba.

Tsadar Rayuwa: Kar ku biye wa masu son yin zanga-zanga a Kano – Amb. Ibrahim Waiya

Ya kuma jaddada cewa hadin kan Najeriya ba abu ne da za a iya yin cinikinsa ba.

Bayan afkuwar lamarin, an samu martani da dama daga ‘yan Najeriya daban-daban ciki har da ‘yan adawa.

BBC Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...