Daga Rahama Umar Kwaru
Wata Kungiya mai suna Kano Coalition For Awareness on Accountability, ta musanta zargin cewa hukumar da ke kula da harkokin fitar da kayayyaki ta kasa (NEPZA) a jihar Kano, ta yi sakacin da ya jawo asarar biliyoyin Naira na kudaden shiga.
Kungiyar, a cikin wata sanarwa da shugabanta Sadi Tanko Surajo ya fitar kuma ta aikewa manema labarai a Kano, sannan ta bayyana zargin a matsayin mara tushe da kuma yunkurin bata sunan ‘yan kasuwa a jihar.
Kwankwaso ya bayyana wadanda suka hana gwamnan Kano sakat tsawon Shekara Daya
“Babu wani abu mai kama da ana yin sakacin a Cibiyar ciniki ba tare da tsangwama ta Kano ba, na shafe shekaru 10 ina gudanar da sana’ata a can, kuma duk zarge-zargen da na karanta a na yi musu, babu wanda zai iya tabbatar da shi”.
Lokaci ya yi da za mu bayyana wa mutane gaskiya kan lamarin. Ina kara maimaita wa, babu wani abu da ake yi da ya saba wa doka a Kano Free trade zone”.
Wannan dai ba shi ne karon farko da ake irin wannan zargi ba, kuma har yanzu hukumomi ba su gano wani abu da ake yi wanda ya sabawa doka a Cibiyar ciniki ta Kano ba. ” Yace