Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya Gana da Nuhu Ribado

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gana da babban mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu a Abuja.

Cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafukansa na sada zumunta ya ce ya yi muhimmiyar ganawa da Nuhu Ribadun.

Kawo yanzu dai ba a san abin da mutanen biyu suka tattauna ba, sai dai wasu na ganin ganawar ba ta rasa nasaba da rikicin masarautu da ake yi a Kanon.

Rikicin Masarautar Kano: Sarkin Musulmi ya Gargadi Malaman Kano

A ƙarshen makon da ya gabata ne mataimakin gwamnan Kano, Comr. Aminu Abdulsalam ya zargi Nuhu Ribadun da kitsa komawar sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero zuwa birnin, kwana biyu bayan da gwamnan jihar ya sanar da tuɓe shi daga sarauta.

Daga yau na fice daga Kannywood – Malam Ali na Kwana chasa’in

Sai dai ofishin Ribadun ya musanta zargin tare da barazanar maka mataimakin gwamnan a kotu idan bai janye kalaman nasa ba.

Daga bisani dai mataimakin gwamnan ya janye kalaman nasa tare da bai wa Ribadu haƙuri, yana mai cewa da farko ba su fahimci yadda batun yake ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...