Hukumar Hisbah a Kano ta kama maza da mata 20 da ke yin wanka tare

Date:

Daga Isah Ahmad Getso

 

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ce ta kama wasu Matasa maza da mata guda 20 bisa laifin yin wanka tare.

Jami’an rundunar ‘Operation Kau Da Badala’ sun kama su ne a wani wurin shakatawa da ke kan titin ring road sakamakon korafin da mazauna yankin suka yi.

Hasashen yanayin da zai kasance yau talata a birnin Kano da wasu jihohin Nigeria

Mataimakin babban kwamandan hukumar, Dakta Mujahidin Aminuddin Abubakar, ya ce laifin ya saba wa dokar Hisbah domin ta hana hada maza da mata a cikin ruwa domin yin wanka.

Hajj 2024: Gwamna Yusuf ya kara goron Sallah ga mahajjatan Kano

Ya nuna damuwarsa kan lamarin, Inda ya ce kamata yayi wanda a cewarsa, za a iya maye gurbinsa da wani aiki mai fa’ida da zai samu lada a wajen Ubangiji.

Ya ce idan an kammala bincike za a hukunta wadanda ake zargin, sannan ya yi kira ga iyaye da su rika sanya ido sosai kan harkakin ‘ya’yansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...