Daga Sani Idris Maiwaya
Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince gwamnatin jihar ta ware Naira miliyan dubu 5 domin biyan hakkokin yan fansho da suka yi ritaya.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a farko wannan shekarar gwamnatin ta biya Naira miliyan dubu 10, Inda ka biya hakkokin kananan ma’aikata da suka gama aiki.
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya furta hakan ne a Zaman majalisar zartaswa karo na 14 da ya jagoranta.
Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya Sauke Shugaban Hukumar Haraji Tare da Nada Sabo
“Ina farin cikin sanar da ku cewa mun sahale a fara biyan kashi na biyu na ma’aikatan da suka yi ritaya gratutinsu a jihar Kano” . A cewar Gwamnan
Gwamna Yusuf ya ce tuni aka ware naira miliyan dubu biyar (5 Billion) domin fara biyan kudaden.