Ƙungiyar Sawaba Initiative ta shirya Taron magance cin hanci da rashawa a Kano

Date:

Daga Aliyu Sufyan Alhassa

 

Ƙungiya Sawaba Initiative for humanitarian Development ta gudanar da taron ta karon farko a jihar Kano, domin tattauna hanyoyin da za a magance cin hanci da rashawa a tsakanin shugabanni.

Ƙungiyar ta jaddada cewar matakin yakar cin hanci da rashawa wani lamari ne da ka iya zama barazana ga goben Najeriya matuƙar ba a kai ga takawa lamarin birki ba.

Hasashen yanayin da za’a tashi da shi gobe talata a Birnin Kano da wasu jihohin Nigeria

Shugaban kungiyar na Kano Comrade Tasi’u Tarauni ya ce ƙungiyar tana da rassa a sassan jihohin Najeriya, inda kuma za su gudanar da taro makamancin wannan a jihohin don tabbatar da an samu raguwar cin hanci da rashawa a tsakanin al’ummar Najeriya.

Abubuwan da ya kamata yan Arewa su yi don amfana da mulkin Tinubu – Kwankwaso

Taron ya samu halartar shugaban hukumar karɓar korafi da yaki da rashawa ta jihar Kano Barrister Muhuyi Magaji Rimin Gado, da shugaban hukumar EFCC mai kula da shiyyar kano da Jigawa, sai wakilcin kwamandan hisba na jihar Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da wakilin Kwamishinan yan sanda na Kano da makamantansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...