Yan Sanda Sun Kama Wanda Ya Kai Harin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna

Date:

 

Daya daga cikin ’yan bindiga da suka kai hari tare da sace fasinjoji a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ya shiga hannu bayan shekaru biyu da faruwar lamarin.

Idan dai za a iya tunawa, a shekarar 2022 ne ’yan bindiga suka kai harin bom kan jirgin, suka yi awon gaba da mutane da dama tare da kashe wasu.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta ce dan ta’addan mai suna Ibrahim Abdullahi, ya shiga hannun jami’anta na yaki da masu garkuwa da mutane ne a ranar 12 ga watan Junairu, 2024 a jihar Kaduna.

 

Kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce, Ibrahim wanda aka fi sani da Mande, ya amsa cewa shi ne shugaban kungiyar masu garkuwa da mutane da ke addabar babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.

NAWOJ ta yi alkawarin hada kai da ma’aikatar tsaro don magance ta’addanci a Nigeria

ACP Adejobi ya ce, “Mande ya amsa cewa shi ne shugaban kungiyar masu garkuwa da mutane da ke addabar babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.

“Yana cikin manyan ’yan ta’adda irin su Dogo Gide da Bello Turji.

“Yana da hannu wajen yin garkuwa da mutane, ciki har da daliban Jami’ar Green Field.

“Ya kasance yana da hannu a kusan dukkanin sace-sacen da ake yi a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Rundunar Sojin Sama Ta Yabawa Dabarun Gwamnan Yusuf Na Yaki Da Barazanar Tsaro A Kano

“Haka zalika da shi aka kai harin jirgin kasa na Kaduna zuwa Abuja amma ya gudu.

“Mun yi wa ’yan Nijeriya alkawarin cewa za a kama shi,” kuma yanzu ya shiga hannu rundunar, in ji shi.

ACP Adejobi ya gabatar da Mande tare da wasu mutane sama da 30 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.

Ya kuma yi nuni da cewa, tsare-tsaren tsaro da aka aiwatar a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna sun taimaka matuka wajen samun nasarori.

Ya ce bisa umarnin shugaban ’yan sanda, an tura jirgi sama mai saukar ungulu ya rika yin sintiri domin taimakawa ta sama ga sojojin kasa daga sojoji, ’yan sanda, da sauran jami’an tsaro da ke kan hanyar jirgin kasan.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...