Sojojin sun kammala bincike kan kisan da aka yi wa masu maulidi a Tudun Biri

Date:

Hedikwatar tsaron Najeriya ta ce ta kammala binciken da aka daɗe ana dako kan bam ɗin da aka jefa kan mutane a ƙauyen Tudun Biri a ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna.

Ta kuma ce sojojin da aka samu da laifi a kai harin za su gurfana a gaban kotun soji domin fuskantar hukunci.

Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron, Edward Buba ne ya bayyana haka a taron yaɗa labaran da aka gudanar a Abuja.

Hajjin Bana: NAHCON ta bayyana ranar da zata fara jigilar alhazan Nigeria

A Disambar bara ne wani jirgin sojoji ya jefa bam kan mutanen da ke bikin maulidi lamarin da ya janyo asarar rayuka da jikkatar wasu da dama.

Rundunar sojin Najeriya ta ɗauki alhakin kai harin inda ta ce lamarin ya faru bisa kuskure.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...