Kamfanonin Sadarwa na neman izinin kara kuɗin kiran waya a Nigeria

Date:

Daga Ibrahim Husaini Dorayi

 

Kamfanonin sadarwar da ke aiki a Najeriya musamman Glo, MTN, Airtel da 9Mobile suna rokon gwamnatin tarayya da ta sahalle musu su kara kuɗin kiran waya domin bunkasa aiyukan su.

A cewar kamfanonin farashin da ake amfani da shi a yanzu bai dace da yanayin tattalin arziki da ake ciki, don haka suke neman izinin gwamnati don kara kuɗin kiran wayar.

Kamfanonin sadarwa guda hudu sun ce su kadai ne ba su kara kudi akan al’amuran su ba wanda hakan ke barazana ga dorewar masana’antar da kuma yiyuwar sanyaya gwiwar masu zuba jari.

Sanarwa ta Musamman Daga Hukumar Samar da Ruwan sha ta Jihar Kano

Sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da kungiyar masu lasisin sadarwa ta Najeriya (ALTON) da kungiyar kamfanonin sadarwa ta Najeriya (ATCON) suka fitar ranar Alhamis.

Tsakananin zafi: Hukumomi a Kano sun ba da shawarwarin kare kai ga al’umma

A cewar sanarwar mai dauke da sa hannun shugaban ALTON, Mista Gbenga Adebayo, da shugaban ATCON, Mista Tony Emokpere, ba a yi wani kari kan farashin kiran waya na bai daya ba a cikin shekaru 11 da suka gabata.

Sun danganta rashin kara kuɗin kiran ga ka’idojin da aka gindaya musu duk da mummunar matsalar tattalin arziki da ake fuskanta a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...