Yanzu-yanzu: Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun hutun karamar Sallah

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Talata da Laraba 9 da 10 ga Afrilu, 2024 a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah karama.

Kadaura24 ta rawaito Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar, Aishetu Ndayako ya fitar ranar Lahadi.

Ministan ya taya daukacin al’ummar musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan mai alfarma lafiya.

Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi Sun Magantu Kan Labarin Rasuwarsa

Tunji-Ojo ya yi kira gare su da su yi koyi da kyawawan dabi’u da halaye na kyautatawa, soyayya, hakuri, zaman lafiya, tausayi, irin na Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi misali da shi.

Dan majalisar dokokin jihar kano Ibrahim kundila ya rasu

“Ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da hadin kai domin ingantawa da samun zaman lafiya da hadin kai a kasar.

“Ministan na yiwa daukacin al’ummar musulmi barka da Sallah tare da addu’ar Allah ya karɓi ibadun da al’ummar musulmi suka yi a cikin watan na azumin Ramadan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...