Kebbi: Gidauniyar IGE BABA DAGGI ta rabawa mutane 600 dubu 10 -10

Date:

Daga Umar Sani Kofar Na’isa

 

Gidauniyar IGE BABA DIGGI karkashin jagorancin shugaba Alhaji Umar Namashaya Diggi ta rabawa al’ummar karamar hukumar Kalgo Tallafin kudi Naira dubu goma goma ga mutane dari shida a garin Diggi.

Shugaban kwamitin rabon tallafin kudin Alh Altine Dandiggi yace manufar shirin zakulo mutane 600 domin a basu kudi hannu don rage musu radadin a wannan wata mai alfarma.

Ku Fara Neman Watan Shawwal A Gobe Litinin – Sarkin Musulmi Ga Musulmin Nigeria

A jawabin wakilin kantoman karamar hukumar mulki ta kalgo Alh Alu Diggi da wakilin ubankasar Diggi Alh Yusuf Aliyu sun yabawa gidauniyar bisa wannan aikin alheri don haka suka yi kira ga masu hannu da shuni suyi koyi da wannan abin alheri.

Ramadan: Abubuwan da ya kamata ku sani game da Khatamar Al-Qur’ani ta bana a masallacin Harami

A nasa jawabin Shugaban gidauniyar Alh Umar namashaya diggi yayi alkawarin cigaba da wannan rabon tallafin kudin lokaci bayan lokaci domin jin kan alummar karamar hukumar Kalgo.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana sun godewa gidauniyar bisa wannan tallafin kudi da aka basu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...