Matsin Rayuwa: Jama’a Sun Daka Wawa a Rumbun Gwamnatin Najeriya

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Jama’ar gari sun fasa wani rumbun ajiyar hatsin gwamnati da ke Abuja, inda suka wawushe kayan abincin da ke ciki.

Da sanyin safiyar Lahadi ne bata-garin suka yi dirar mikiya suka balla rumbun ajiyar abincin da ke garin Gwagwa, suka fara awon gaba da hatsin ciki.

Mazauna yankin sun ce bata-garin sun isa rumbun abincin da ke yankin Tasha ne da misalin karfe 7 na safe, suna kinkimo buhunan abincin da ke dauke da tambarin Gwamnatin Tarayya.

Sulhu: Gwamnan Kano Abba Kabir Ya Gana da Sheikh Daurawa

Wani mazaunin unguwar Karmo da ke kusa da wurin mai suna Ja’afar Aminu ya ce an shafe sama da awa biyu ana kwasar kayan abinci daga dakin ajiyar.

A cewarsa, mazauna Karmo da makwabtansu daga yankin Jiwa suna tururuwar zuwa kwasar abincin, lamarin ya haifar da cinkoson ababen hawa a kan hanyar Gwagwa zuwa Karmo zuwa Jabi da Dei-Dei.

Ja’afar ya ce shi kansa yi kokarin zuwa wurin amma ya hakura, saboda raunukan da ya samu a yamutsin.

Wani mazaunin Karmo, Christopher Agbo, ya ce wasu daga cikin dandazon mutanen da suka yi wa wurin dirar mikiya suna rika yin awon gaba da karafunan da ke wurin da sauran kayan gwangwan.

Shi ma wani dan unguwar da ya ce ya hadu da mutane dauke da buhunan hatsin, Sani Yusuf, ya ce mutanen suna kokawa da cewa kayan abincin ba za su ciwu ba, domin sun riga sun rube.

Iftila’i: Cutar kyanda ta barke a Kano

Wasu daga cikin matasan sun nufi rukunin masana’antu na Idu da ke Abuja, inda kamfanoni ke da rumbunan ajiya, ciki har da wadanda gwamnati ta kama haya domin adana.

Sai dai wakilinmu ya tuntubi mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Abuja, Josephine Adeh, wadda ta shaida masa cewa sun samu rahoton abin da ke faruwa kuma tun sun tura jami’ansu domin shawo kan lamarin.

Irin haka ta faru da kayan tallafin a lokacin annobar COVID-19 a Abuja, inda bata-gari suka far wa rumbuna ajiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...