Rundunar Yan Sandan Kano ta Bayyana Shirin ta Kan Ziyarar Matar Tinubu

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta tabbatar da cewa ta shirya tsaf ta fuskar samar da tsaro domin ziyarar aiki da uwargidan shugaban kasa, Oluremi Tinubu ta kai jihar a ranar 12 ga watan Fabrairu.

Kwamishinan ‘yan sandan, Hussaini Gumel, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a Kano.

Gumel ya ce sun samar da isassun jami’an tsaro wadanda suke cikin shiri domin tabbatar da uwar gidan shugaban kasa ta kammala ziyarar da zata kawo kano lami lafiya .

Tsadar Rayuwa: Abubuwan da Ɗangote yayi alkawarin taimakawa al’ummar Kano da su

Gumel ya ce rundunar ta dauki kwararan matakan tsaro domin tabbatar da ziyarar lafiya.

“Mun tattara isassun jami’ai masu dauke da makamai domin baiwa uwargidan shugaban kasa kariya kafin ziyarar, da lokacin da kuma bayan ziyarar,” in ji Gumel.

Kwamishinan ya kuma ce tuni rundunar ta fara shirin “Operation Show Force” tare da sauran jami’an tsaro domin nuna shirin su kan ziyarar uwar gidan.

Tinubu Ya Bayar da Sabon Umarni ga Yan Nigeria

Ya bayyana cewa an dauki matakan ne domin baiwa mazauna jihar damar tarbar uwargidan shugaban kasar da mukarrabanta ba tare da wata barazana ta tsaro ba .

Kwamishinan ya shawarci shugabannin jam’iyyun siyasar jihar da su ja hankalin magoya bayansu da su nisanci duk wani nau’in tashin hankali da ‘yan daba kafin ziyarar uwargidan shugaban kasa da kuma bayan ziyarar.

Gumel ya ce: “Ba za mu amince da duk wani aiki da zai kawo rudani kafin ziyarar, lokacin da kuma bayan ziyarar ba.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...