Yanzu-yanzu INEC ta Bayyana Dalilan ta na Dkatar da Zaɓen Kunchin da tsanyawa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bada sanarwar soke dakatar da zaben dan majalisar jihar da Ake sakewa a yankin kananan hukumomin Kunchi da tsanyawa a jihar Kano.

“Mun dakatar da zaɓen da yake gudanar yanzu haka a mazabu goba na karamar hukumar kunchi sakamakon yadda yan daba suka lalata kayan aikin zaɓen”.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan hulda da Jama’a da wayar da kan masu zaɓen na hukumar Sam Olumekun ya sanyawa hannu .

Zaben Cike Gurbi: INEC ta Magantu Kan Sace Akwatunan Zabe a Kano

Sanarwar tace matakin dakatar da zaɓen yayi daidai da sashi na 24 (3) na dokar zabe ta 2022. “zamu sanar da mataki na gaba da zamu dauka bayan gama ganawa da masu ruwa da tsaki na hukumar a ranar litinin”.

Sanarwar dakatar da zaɓen ta shafi zaɓen da ake gudanar a wasu mazabu a jihohin Akwa Ibom da Enugu.

INEC ta kuma bukaci jami’an tsaro da su gudanar da bincike kan lamarin, yayin da ta ce ita na zata gudanar da bincike don tabbatar da ko akwai sakacin ma’aikatan ta

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...