Kotu ta yi wa mutum biyu ɗaurin rai-da-rai a kan laifin luwaɗi da yara a Jigawa

Date:

Wata babbar kotun jihar Jigawa da ke zama a Dutse karkashin jagorancin Mai shari’a Muhammad Abubakar Sambo ta yanke wa Isah Haruna hukuncin ɗaurin rai-da-rai bayan samunsa da laifin yin luwaɗi.

An gurfanar da wanda ake tuhumar ne ranar 2 ga watan Mayun 2023, bisa zargin aikata fyaɗe, lamarin da ya saɓa wa sashe na 3 na dokar hana cin zarafin lalata ta (VAPP) a jihar Jigawa 2021.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a ranar 10 ga watan Yunin 2022, wanda aka yanke wa hukuncin ya yaudari wani yaro ɗan shekara 14 a wani kanti da ke Gwaram Sabuwa, a karamar hukumar Gwaram a jihar Jigawa, inda ya yi luwaɗi da shi.

Lauyan mai shigar da ƙara, Sunusi Sani, ya gabatar da shaidu biyar a kan wanda ake kara, shi kuma wanda ake kara ya bayar da shaida don kare kansa.

A karon farko Jaruma Khadija Mainumfashi ta Magantu kan dakatarwar da gwamnatin Kano ta yi mata

Alkali mai yanke hukunci, ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da dukkan hujjoji da suka nuna cewa wanda ake ƙara ya aikata luwaɗi, inda ya yanke wa Isa Haruna hukuncin ɗaurin rai-da-rai.

A wani hukunci kuma, babbar kotu mai lamba 6 da ke zamanta a Birnin Kudu a karkashin Mai shari’a Musa Ubale, ta samu wani Ibrahim Sani da ke kauyen Kiyako na karamar hukumar Birnin Kudu da laifin luwadi da yara, inda ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai.

An gurfanar da wanda ake tuhumar ne a gaban kotu, bisa tuhuma shida da suka haɗa da luwadi.

Ana zarginsa da yin luwaɗi da wasu yara maza shida masu shekaru tsakanin 11 zuwa 16, laifin kuma da ya saɓa wa sashe na 284 (1) na kundin laifuka wanda aka yi wa gyara na 2014.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...