Hukumar tace fina-finai ta Kano ta Bayyana Dalilan ta na dakatar da Jarumi Malam Ali na kwana 90

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

 

Hukumar Tace Fina-finai ta Kano ta dakatar da Jarumi Abdul Saheer da aka fi sani da Malam Ali Kwana Casa’in daga Fina-finan Hausa har tsahon Shekaru biyu.

Hukumar tace hakan ya biyo bayan korafe-korafen da aka yi a kansa na cewa yana yada bidiyon batsa a kafafen sada zumunta.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban hukumar Abba El-Mustapha ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a ofishinsa dake kano.

Talla

Abba El-Mustapha yace Hukumar su ta gayyaci Jarumi Abdul Sahir domin ya amsa tambayoyi kan zargin da ake masa na yada bidiyon batsa, amma ya bijirewa amsa gayyatar .

” Abun da Jarumi yayi na kin amsa gayyatar da mukai masa na zuwa gaban hukumar da karfe 10 na safiyar yau ( Litinin) ya nuna cewa yayi abun da yayi don ya ci mutuncin al’ummar jihar kano da kuma zubar da kimar ta”. El-Mustapha

Yadda tattaunawar hukumar Hisbah ta kasance da Yan Kannywood

Shugaban hukumar tace fina-finai ya kuma yi kira da dukkanin masu shirya fina-finai da su guji sanya Jarumin a fina-finan su har sai wa’adin da hukumar ta sanya masa na shekaru biyu ya cika.

” Haka zalika Muna kira ga kafafen yada labarai da su daina gayyatar Jarumi Abdul Sahir wadanda aka fi sani da Malam Ali don yin hira da shi akan duk abun da ya Shafi harkokin fina-finai”. Inji Abba El-Mustapha

Abba El-Mustapha ya kuma bukaci duk wadanda dama sun sanya Jarumin a fina-finan su amma basu saki fim din ba ,da su hanzarta Kai fina-finan na su Cikin sati biyu domin tantancewa. Sai dai yace duk wanda ya wuce sati biyu bai kai fim din sa ba to ya sani ba zasu saurare shi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...