Fagen yada labarai na zuwa da sabon Ilimi, shi yasa muke inganta fannin – Gwamnatin Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mataimakin gwamnan jihar kano Kwamarat Aminu Abdulsalam Gwarzo ya bukaci yan jaridu da jama’an yada labarai su rika rungumar sauyin da ake samu a faggen yada labarai koda yaushe.

Cigaban da ake samu mai dauke da kalubale da yawa a aikin jarida ke kawo barazana ga ma’aikata, don haka nake kira ga duk wani jami’in yada labarai tun daga matakin farko a karatu zuwa makura, ko wadanda suka dauki tsawon shekaru a aikin, wajibi su yadda cewa fagen aikin yada labarai fage ne dake zuwa da sabon ilimi a Koda yaushe”.

Talla

Mataimakin Gwamnan jihar kano kwamarad Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya bayyana haka yayin bitar kwanaki shida da ma’aikatar yada labarai ta shirya ga jami’anta na kanan hukumomi 44 a jihar Kano.

Kwamarad yace Akwai bukatar jami’an yada labarai su zama masu bibiya, karance-karance, shiga shafuka da kuma halartar bita don karawa Juna sani domin su inganta aikinsu, jin ilimi ya ishi mutum ko gadara da dadewa cikin aikin zai iya sawa a bar mutum a baya .

Tinubu ya naɗa sabbin kwamishinonin zaɓe a jihohi tara

Wasu Daga Cikin mahalarta bitar daga wasu kananan hukumomin sun bayyana gamsuwa da abubuwa da aka koya musu kan sha’anin yada labarai, daga bisani suka mika godiyarsu ga gwamnan jihar kano dama kwamishinan yada labarai daya jajirce wajen tabbatar da wannan bita.

Dayake jawabi kwamishinan yada labaran da harkokin cikin gida na jihar Kano, Baba Halilu Dantiye MON MNI, ya shaida cewa yana da yakinin jami’an da aka baiwa bita zasu kara inganta aikinsu don dama sun iya, sannan kashin farko ne suka kammala inda aka kawo kwararrun masu bada horo a fannoni daban – daban.

Dan tiye ya tabbatar da cewa za suyi kundi su mayar da da duk takardun da aka gabatar Littafi Domin ya zama tarihi ga Mutane Baya, don su ma su amfana .

Talla

kwamishina yace baya ga jami’an yada labaran, gwamnatin jihar kano zata shirya irini wannan bita ga masu bada rahoto na musamman da Gwamna ya dauka, da ma’aikatan radio na gwamnati da masu zaman kansu don kara inganta harkokin yada labarai a jihar kano.

Kimanin jama’ai yada labarai 214 ne rukunin farko suka rabauta da bitar daga ofisoshin yada labarai na kanan hukumomi 44, da ma’aikatar yada labarai baki daya kamar yadda Gwamnan Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya dauki nauyi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...