Jarumi Aki ya bayyana dalilin da ya sa yake boye matarsa da ‘ya’yana ga shafukan sada zumunta

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Fitaccen jarumin fina-finan Nollywood, Chinedu Ikedieze, wanda aka fi sani da Aki, ya bayyana dalilin da ya sa baya bari a ga iyalansa a shafukan sada zumunta.

 

Jarumin mai shekaru 45 a duniya ya ce ba ya so matarsa ​​da ‘ya’yansa su shiga shafukan sada zumunta saboda yana son su sami ‘yanci.

Talla

Ya bayyana hakan ne a wata hira da yayi da manema labarai .

Ya ce, “Ina da ‘ya’ya amma na yanke shawarar ajiye su a gefe saboda ni ne shahararren, ba su ba.

ECOWAS ta Sanya Ranar da Zata Fara Yakar Jamhoriyyar Nijar

“Ina so kawai su sami ‘yanci saboda duk lokacin da kowa ya san su, zai shafe su, kuma hakan zai sa su rasa ‘yanci, Kuma ba na son hakan.

“Don haka, na boye su har da matata, in ban da a sanarwar bikin aurenmu da aka ganta, kuma daga nan ba a kara ganin ta ba, hakan tasa take iya zuwa kasuwa, ta yi duk abun da take bukatar cikin yanci ba kamar ni ba.”

KADAURA24 ta tuna cewa Ikedieze ya auri masoyoyarsa Nneoma Nwaijah a shekarar 2011.

Ma’auratan sun haifi ‘ya’ya amma dan wasan ya yanke shawarar ɓoye takamaiman adadin ‘ya’yan

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...