Ƴan majalisa a Ghana sun gargaɗi shugaban ƙasar kan tura sojoji Nijar

Date:

Ƴan majalisa ɓangaren marasa rinjaye a Ghana sun nuna adawa kan matakin da Ecowas a ɗauka na shirin afka wa Nijar a matsayin wani yunkuri na dawo da mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.
Nijar.

“Majalisar dokokin Ghana ba ta tattauna ba kan lamarin kamar yadda sauran ƙasashe suka yi har ma da ɗaukan mataki, in ji Samuel Ablakwa, wani ɗan majalisa a kwamitin kula da harkokin ƙasashen waje.

Talla

Ƴan majalisar sun gargaɗi Shugaban ƙasar, Nana Akufo-Addo cewa ya dakatar da shirin tura sojojin ƙasar domin zuwa

Ya ce Shugaba Akufo-Addo ba sai ya ji ta baki ƴan ƙasar Ghana ba kan lamarin , saboda tura sojoji Nijar ba shi ne mafita ba.

Dalilai Guda 10 da DSS ta bayar kin Amincewa da El-Rufai a matsayin Ministan Tinubu

BBC ta rawaito yan majalisar ƙasar ɓangaren marasa rinjaye sun ce abin da ya kamata a yi shi ne bin hanyar diflomasiyya da kuma tattauna.

“Ba abu mai kyau bane tura sojojin Ghana zuwa Nijar domin zub da jini, kuma muddin ba a yi hankali, abin zai sake jefa yankin cikin tashin hankali,” in ji Mista Ablakwa.

Ƴan majalisar sun ce ya kamata a yi amfani da kuɗin da ake da shi wajen warware matsin tattalin arziki da ƙasar ke fusknta baya nciyo rancen $3b daga Asusun IMF maimakon tura sojoji zuwa faɗa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...