Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Kotun sauraron kararrakin zaben yan majalisar tarayya dake kano ta soke zaben da aka yiwa Hon. Mukhtar Yarima na jam’iyyar NNPP a matsayin Danmajalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Tarauni.
Yarima dai shi ne ya tsayawa jam’iyyar NNPP a zaben da akayi a watan Fabarerun daya gabata.

Kotun mai alkalai uku, ta tabbatar da Hon Hafiz Ibrahim Kawu na Jam’iyyar APC a matsayin wanda ta mikawa kujerar bisa dogaro da hujjar gabatar da sakamakon bogi na Firamare da Dan majalisar Yarima yayi.