Sarki Sanusi ya yi wa Tinubu karin haske, bayan ganawa da shugaban mulkin soji na Nijar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A daren jiya Laraba ne Sarkin Kano na 14, Alhaji Muhammadu Sanusi ya ziyarci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

 

Sarki Sanusi ya isa fadar Villa ne da misalin karfe 8:25 na dare bayan wata babbar tawagar Malamai ta Najeriya data gana da shugaban kasar.

 

Tsohon Sarkin dai ya dawo ne daga Jamhuriyar Nijar inda ya gana da gwamnatin mulkin soja da ta kwace mulki daga hannun zababben shugaban kasar Mohamed Bazoum.

Talla

Kadaura24 ta ruwaito yadda Sanusi ya gana da shugabannin da suka yi juyin mulki Inda suja tattaunawa kan abun da ya shafi juyin mulkin.

 

Wasu majiyoyi sun shaida wa jaridar Daily trust cewa Sanusi ya je Nijar din ne a radin kansa, amma gabanin tafiyarsa ya sanar da shugaba Tinubu .

Juyin Mulkin Nijar: Muhammad Bazoum ya bayyana halin da ya shiga a hannun sojojin Nijar

Tawagar da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS basu sami ganawa da shugabannin sojojin ba saboda sun ki yadda sa gana da su.

Amma a ranar Laraba, Hotunan Sanusi wanda shi ne shugaban Darikar Tijjaniya a Nigeria dake da dimbin magoya baya a Nijar, sun karade shafukan sada zumunta. shiga yadu.Sanusi shi ne Khal

Yayin ganawar Sanusi da Shugaban Mulkin Soji na Nijar yana tare da Sultan na Damagara,, wanda Damagaran shi ne birni na uku mafi girma a Nijar.

Majiyoyi sun shaida wa Daily trust cewa Sanusi ya je Nijar din ne domin ya bude kofa tattaunawa da gwamnatin mulkin soja. Daya daga cikin majiyar ta ce, “Mai martaba ya yi wannan tafiya ne a radin kansa, amma ba da sanin shugaban kasa Bola Tinubu ne biyo bayan damuwarsa game da rikicin da ake yi da kuma yadda za a shawo kan matsalar.

Taron ya zo kwana guda gabanin taron shugabannin ECOWAS a Abuja Tinubu, wanda shi ne Shugaban ECOWAS, ya shirya wani taro a ranar Alhamis bayan wa’adin kwanaki 7 da kungiyar ta fitar na maido da Bazoum mulkin kasar ya cika.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...