Juyin Mulki: Shugabannin kungiyar ECOWAS na ganawa kan matakin da zasu dauka a Nijar

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS na gudanar da wani taro yau Alhamis a Abuja kan halin da ake ciki a jamhuriyar Nijar.

 

Shugabannin za su yanke shawara kan matakin da za su dauka na gaba bayan jerin shawarwari da suka baiwa gwamnatin mulkin soja a Nijar na maido da mulkin dimokuradiyya a Kasa.

Talla

Shugaba Bola Tinubu, wanda shi ne shugaban kungiyar ECOWAS a halin yanzu yana karbar bakuncin shugabannin a fadar gwamnatin tarayya.

 

Wani fitaccen hukunci da aka yanke a baya a kan shugabannin shi ne yin amfani da karfin soji, bayan wa’adin kwanaki bakwai da aka baiwa gwamnatin mulkin da ta hambarar da shugaba Mohamed Bazoum.

Dogaro da kai: Falakin Shinkafi ya ɗauki nauyin koyawa Daliban makarantar Shekara 230 Sana’o’i

Kwanaki shida bayan bikin ranar 26 ga watan Yuli, shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS a wani taro da suka yi a Abuja, sun yi kira da a gaggauta sakin Bazoum a matsayin halastaccen shugaban kasa da gwamnatin Jamhuriyar Nijar.

Shugabannin sun yi kakkausar suka kan juyin mulkin da aka yi a Nijar, da tsare Bazoum ba bisa ka’ida ba, da kuma ‘yan uwa da gwamnatinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...