Juyin Mulki: Shugabannin kungiyar ECOWAS na ganawa kan matakin da zasu dauka a Nijar

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS na gudanar da wani taro yau Alhamis a Abuja kan halin da ake ciki a jamhuriyar Nijar.

 

Shugabannin za su yanke shawara kan matakin da za su dauka na gaba bayan jerin shawarwari da suka baiwa gwamnatin mulkin soja a Nijar na maido da mulkin dimokuradiyya a Kasa.

Talla

Shugaba Bola Tinubu, wanda shi ne shugaban kungiyar ECOWAS a halin yanzu yana karbar bakuncin shugabannin a fadar gwamnatin tarayya.

 

Wani fitaccen hukunci da aka yanke a baya a kan shugabannin shi ne yin amfani da karfin soji, bayan wa’adin kwanaki bakwai da aka baiwa gwamnatin mulkin da ta hambarar da shugaba Mohamed Bazoum.

Dogaro da kai: Falakin Shinkafi ya ɗauki nauyin koyawa Daliban makarantar Shekara 230 Sana’o’i

Kwanaki shida bayan bikin ranar 26 ga watan Yuli, shugabannin kasashen kungiyar ECOWAS a wani taro da suka yi a Abuja, sun yi kira da a gaggauta sakin Bazoum a matsayin halastaccen shugaban kasa da gwamnatin Jamhuriyar Nijar.

Shugabannin sun yi kakkausar suka kan juyin mulkin da aka yi a Nijar, da tsare Bazoum ba bisa ka’ida ba, da kuma ‘yan uwa da gwamnatinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...