Hajjin bana: Hukumar jin dadin alhazai ta Kano ta bada tallafin kudi da kayan abinci ga iyalan Alhazan da suka rasu

Date:

Daga Ibrahim Abubakar Diso

 

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar kano ta kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan wasu alhazai da suka rasu a kasa mai sarki yayin gudanar da ibadar aikin hajjin bana.

 

Kadaura24 ta rawaito Babban daraktan hukumar Alh , Laminu Rabiu Danbappa shi ne ya jagoranci tawagar daraktoci hukumar domin zuwa taaziyar.

Talla

Tunda fari dai tawagar ta ziyarci kauyen gago Rikadawa dake karamar hukumar Madobi inda aka yiwa iyalam Hajiya Hadiza Ismail ta’aziyya , bayan nan aka gabatar musu da kayan abinci da kudi wanda hukumar ta bayan ga iyalan marigayiyar.

 

A jawabin shugaban hukumar Alh. Laminu Rabi’u, yace marigayiyar ta rasu a birnin Makka kuma anyi mata sallah a masallacin Harami, sannan yayin musu ta’aziyya tare da yiwa mamaciyar addu’o’in samun rahamar Allah (S W A).

Juyin Mulkin Nijar: Muhammad Bazoum ya bayyana halin da ya shiga a hannun sojojin Nijar

Daya daga cikin dangin marigayiyar yace murgayiyar bata da da ko jika , amma ya nemi gwamnatin jiihar kano data yi musu rijiyar burtsatse domin a cigaba da tunawa da murgayiyar,kuma nan take Alh Laminu Rabiu ya amsa wannan bukata.

Daga bisani tawagar ta kai ziyara Garin Rimin Gado domin yin ta’aziyya ga iyalan mai unguwa Dan Azumi mai unguwar Zangon Dan Audu dake Rimin Gado wanda shi ma Allah ya karbi ransa a kasa mai sarki bayan gajeriyar jinya da yayi fama da ita, inda anan ma aka gabatar a addu’a ga mamacin sannan aka mika musu abinci da kudi.

Shugaban Majalisar Dattawan Nigeria ya yi subul da baka an wasu kudade

Haka zaluka tawagar takai ta’aziyya ga iyalan margayi, Alh Shitu Inuwa Gunduwawa dake karamar hukumar Gezawa wanda Allah ya karbi ransa a kasa mai tsarki , bayan ya kammala aikin hajjinsa, Babban daraktan hukumar jindadi alhazai ta jihar kano , Alh. Laminu Rabiu Dan bappa ya gabatarwa da iyalinsa kayan abinci da kudi.

Bayan nan tawagar taje karamar hukumar Gaya inda ta gana da iyala Umar Mustapha wanda yake fama da rashin lafiya, inda a yanzu haka yana karbar magani a kasa mai tsarki, Alh. Laminu Rabi’u ya tabbabatarwa da iyalansa cewa da zarar ya dada samun lafiya za a dawo dashi gida Nigeria, sannan ya gabatar musu da kayan abinci da kudi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...