Da dumi-dumi: ECOWAS ta bayyana matakin da zata dauka akan gwamnatin sojin Nijar

Date:

Daga Zainab Kabir Kundila

 

Shugabannin kungiyar ECOWAS sun ba da umarnin gaggauta daukar matakin amfani da karfin soji kan gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar. Sun kuma yi kira ga kungiyar Tarayyar Afirka, AU, da sauransu da su goyi bayan kudurin da kungiyar .

 

Kungiyar ECOWAS ta ce duk kokarin da aka yi na tattaunawa da gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar, shugabannin juyin mulkin sun yi watsi da shi, yayin da suke yin Allah wadai da ci gaba da tsare shugaba Mohamed Bazoum da iyalansa.

Talla

An cimma wannan matsaya ta shugabannin ECOWAS ne a taron koli na musamman kan harkokin siyasa a Jamhuriyar Nijar wanda ya samu halartar shugabannin kasashe takwas da ministocin harkokin wajen kasashen Laberiya da Gambia da aka kammala a Abuja.

Shugaban kasar Mauritania, Mohamed Ould Ghazouani da takwaransa na Burundi, Everiste Ndayishimiye sun halarci taron gaggawa na kungiyar ECOWAS karo na biyu kan Jamhuriyar Nijar bisa gayyatar abokan aikinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...