Da dumi-dumi: Tinubu ya ba da umarnin sake ƙaƙaba wa Nijar takunkumai

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Shugaban kungiyar Ecowas, Bola Tinubu, ya umarci Babban Bankin Najeriya ya sanya ƙarin takunkuman kuɗi a kan hukumomi da ɗaiɗaikun mutanen da ke da alaƙa da shugabannin juyin mulki a Nijar.

 

Matakin na zuwa bayan ƙarewar wa’adin mako ɗaya da ƙungiyar Ecowas ta bai wa sojojin Nijar bisa tanadin yarjejeniyar sanya takunkuman kuɗi na shugabannin ƙasashen ƙungiyar Ecowas.

 

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban na Najeriya shawara na musamman kan harkar yaɗa labarai, Anjuri Ngalale ta ce Tinubu ya umarci gwamnan babban bankin na CBN ya ƙaƙaba wasu jerin takunkumai a kan masu hulɗa da sojojin da ke mulkin Nijar.

Talla

Shugaba Tinubu ya ce bai ɗauki matakin cikin kuskure ba ne, saboda ya samu izini daga takwarorinsa na Ecowas don fitar da sanarwa, ya kuma nanata cewa matsayin, ba al’amari ne da ya ɗauka da sunan wani shugaban ƙasa guda ɗaya ba.

 

Ya ce takunkuman da aka sanya wa Nijar, mataki ne da ya ɗauka a matsayinsa na shugaban Ecowas, kuma shugaban Najeriya, amma yana tsaye a kan ikon da yarjejeniyar ƙudurin dukkan ƙasashe wakilan Ecowas da shugabannin ƙasashen ƙungiyar.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano ya nada mataimaka na musamman guda 42

A cewarsa, matakin iko ne, da ba na gwamnatin Najeriya ba, ƙuduri ne da aka zartar a bainar jama’a kafin wannan lokaci. Shugaban Najeriyar dai yana mayar martani ne ga sukar da yake fuskanta a ciki da wajen ƙasar game da matakin sanya wa Nijar takunkumai da barazanar ɗaukar matakin soji na ƙungiyar Ecowas, bayan hamɓarar da Shugaba Mohamed Bazoum daga mulki.

Tinubu ya ce bayar da wa’adi ga Nijar, hurumin Ecowas ne, ba na Najeriya ba.

Yanzu-Yanzu: Shugaba Tinubu ya gana da Ngozi Okonjo Owela a Abuja

A cewarsa Najeriya, ba ta bai wa Nijar wani wa’adi ba. Sanarwar ta kuma ambato shugaban Najeriyar na cewa a ‘yan kwanakin nan, bayan cikar wa’adin Ecowas, ya faɗada tuntuɓa a ciki da wajen ƙasar ciki har da musayar ra’ayi da gwamnonin jihohi masu iyaka da Nijar dangane da abin da ya faru a maƙwabciyar ƙasar.

Amma Shugaba Tinubu ya nanata ƙudurin cewa duk martanin da Ecowas ta mayar da kuma wanda za ta mayar a kan batun juyin mulkin Nijar, zai kasance ne ba tare da la’akari ko tunanin bambancin ƙabila ko addini ba.

Ya ce ƙungiyar ta ƙunshi dukkan ƙabilu da addinai daban-daban da kuma sauran nau’o’in bambance-bambancen al’ummomin Afirka ta Yamma, don haka martanin Ecowas zai kasance ya yi la’akari da duk waɗannan ɓangarori, amma ba wani daga cikinsu ba.

Ya ce duk da yake babu wani zaɓi da aka ɗauke a jerin matakan da za a iya amfani da su, ƙungiyar za ta gudanar da taron ƙoli a Abuja ranar Alhamis, inda ake sa rai Ecowas za ta cimma muhimman shawarwari a kan matakai na gaba a kan Nijar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...