Daga Isa Ahmad Getso
Manyan hafsoshin soji daga wasu kasashen yammacin Afirka sun isa hedikwatar tsaro da ke Abuja, domin wata ganawa mai karfi kan ayyukan gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar.
Rahotannin da kadaura24 ta samu ya tabbatar da cewa kujerun da aka ware wa shugabannin sojojin Mali da Guinea Bissau da Nijar da Burkina Faso a halin yanzu babu kowa.

Hafsoshin sojojin da ke ganawar a halin yanzu sun hada da na kasashen Togo, Saliyo, Senegal, Nigeria, Ghana, Liberia, Guinea, Gambia, Cote’Divoire, Cape Verde da Jamhuriyar Benin.
Da dumi-dumi: Masu Zanga-Zanga Sun Ɓalle Ƙofar Majalisa
Shugaban kungiyar ta ECOWAS, Janar Christopher Musa ne ke jagorantar taron.
A ranar Lahadin da ta gabata ne kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta bai wa sojojin Nijar wa’adin mako guda su mayar was shugaba Bazoum mukamin sa ko kungiyar ta ɗauki matakin amfani da sojoji akan su .