Inganta Rayuwar matasa : Shekarau ya baiwa gwamnatin tarayya da na jihohi shawara

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, ya bukaci gwamnatocin jihohi da na tarayya da su samar da cibiyoyin koyar da sana’o’i a jami’o’i domin magance matsalar karuwar rashin aikin yi da ya addabi kasar Nigeria.

 

“A kowace shekara jami’o’i da manyan makarantu na yayi miliyoyin wadanda suka kammala karatu ba tare da aikin yi ba, kuma halin rashin aikin yi a Najeriya ya sanya akasarin daliban da suka kammala karatu cikin Takaici”. Inji Shekarau

Talla

Sanata Shekarau, ya yi wannan kiran ne a wajen rufe bikin horas da matasan jahar Yobe sana’oi da gidauniyar Sir Ahmadu Bello, da hadin gwiwar gwamnatin jihar Yobe ta kuma tallafa musu da kudade domin bunkasa sana’o’insu.

 

“A cikin shekaru da yawa da suka gabata, ƙalubalen kasar nan shi ne rashin aikin yi ga matasa, kuma mafita ita ce koma wa kan sana’oi. A yau muna da wadanda suka kammala karatun digiri da digiri na biyu, da Ph.D. Masu yawa wajen neman aikin yi”. A cewar Shekarau

Al’adun Bahaushe: Shin ko kun San Al’adar Bahaushe ta zuwa gida rainon ciki da haihuwa ?

“Sakona ga gwamnatin tarayya shi ne a samar da cibiyoyi a jami’o’i, manyan makarantu Wanda za su bullo da wani bangare na horar da Dalibai sana’oi domin a lokacin da suka kammala karatu a fannoni daban-daban suna da wasu sana’o’in da za su je don fara rayuwa a kansu,”

Tsohon Ministan Ilimi wanda shi ne Sakataren Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello yayi kira ta ga Gwamnatin Yobe, da ma gwamnatocin Jihohin Arewa dasu jajirce wajen kawar da talauci da kuma magance wasu matsalolin da suka addabi yankunan mu.

 

Abin da gidauniyar ke yi a yanzu shi ne Taimakawa Matasa da suke da kwarewa a wani fanni na Sana’a don su samu Dogaro da kai ,tare da kara wayar musu da kai.Don haka na tabbata duk wadanda aka horar za su je su horar da wasu kuma za su kara daukar ma’aikata,” inji Sanata Shekarau

Amfanin Dauɗar Kunne” Da Illar Ƙwaƙwale ta – Daga Masana

A nasa jawabin, Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe, ya ce dole a dawo kan tsari irin nasu Sardauna, a yanzu yankin arewa ya fada cikini talauci sakamakon rashin shugabanci, ga rashawa da rashin shugabanci na gari.

Buni wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Hon Idi Barde Gubana, ya ce domin al’amura su daidaita a yankin ya bukaci yaki da talauci tare da saka jari a fannin ilimi.

Yayin da sauran yankunan kasar ke gudun talauci, jihohin arewa kuma sun rungumi talauci. Muna bukatar abin da zai hada kan Arewa ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasa ko kabila ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...