Mun Gano Kabilanci da Rashin Kuɗi ne yasa Fina-finan Kannywood Basa Karade Nigeria – Ado Gidan Dabino

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa

 

Shugaban kungiyar Masana’antar fina-finai ta MOPAN reshen na jihar Kano  Alhaji Ado Ahmad Gidan Dabino, ya koka da yanayin da masa masana’antar shirya fina-finai Hausa ta kanywood take ciki a nan kano da kuma Arewa cin Nageria .

 

“Daga cikin manyan matsalolin da harkar fim take fuskanta akwai rashin kasuwa yadda ya kamata da kuma masu satar fasaha sai kuma chanza musu ma’anar film dinsu zuwa wata alkibilar ta daban”.

Talla

Kadaura24 ta rawaito Ado Ahmad Gidan Dabino ya bayyana hakan ne yayin wani taro na yini biyu da Kungiyar ta shirya domin duba irin kalubalen da sha’anin harkar fim ke ciki a Arewacin Nigeria.

 

Yace kungiyar MOPAN da sauran masu ruwa da tsari sun bada tabbacin yin duk mai yiyuwa wajen ganin an kawo ƙarshen matsalolin da suka dabaibaye Masana’antar Kannywood da arewacin Nigeria baki daya .

Yunkurin rushe gidaje: Kotu ta ci tarar gwamnatin Kano

Gidan dabino ya kuma musanta zargin da ake yi musu na cewa jarumai da sauran masu harkar fim a Arewacin Nigeria basu da kwarewar da ta dace, wanda hakan ne yasa takwarar fina-finsu basa karade nageria baki daya, sai dai kawai su tsaya a arewacin Nageria .

 

“Kabilancin da suke fuskanta daga gurin abokan sana’ar su na kudancin Nageria ne yasa fina-finan hausa basa iya zuwa har cen kudancin Nigeria, da kuma karanchin kudi ga masu shirya film a Arewacin Nigeria”. Inji Gidan Dabino

 

Gidan Dabino yace zasu ɗauki matakan da suka dace domin magance matsalolin da suke cikin harkar film a jihar kano dama kasa baki daya.

Yace samun cikakken hadin kai tsakaninsu da gwamnati tare kuma da basu damar tantance duk wani film da zai fita bayan an kammala shi kafin fitarsa ga al’umma.

A nasa jawabin Sakataren kungiyar ta MOPAN reshen jihar kano Kamal S Alkali yace a yayin taron an fito da matsalolin Masu tarin yawa da Masana’antar take fuskanta, kuma an bada shawarwarin hanyoyin da za’a bi domin warware su.

Masu ruwa da tsaki a harkar fim a kano da kasa baki daya ne suka sami hallarta taron cikinsu harda shugaban kungiyar MOPAN ta kasa baki daya Alh Ahmad Sarari.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...