Shekarar musulunci: Gwamnatin Kano ta bada hutu ga ma’aikata

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta ayyana gobe Laraba, 19 ga watan Yuli, 2023 a matsayin ranar hutun domin murnar shigowa sabuwar shekara ta Musulunci ta 1445.

Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai na jihar kano Baba Halilu Dantiye a madadin gwamna Abba Kabir Yusif.

 

Gwamnan wanda ya taya al’ummar musulmin duniya murnar zagayowar sabuwar shekara ta Musulunci, ya kuma bukaci ma’aikatan gwamnati da sauran al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya kawo mana zaman lafiya da kwanciyar hankali tare da bunkasa tattalin arzikin jiharmu da kasa baki daya”.

Gwamnan Kano ya nada masu bashi shawara 15

Gwamnan ya kuma yi kira ga al’umma da su rika gudanar da rayuwarsu bisa koyarwar addinin Musulunci tare da yin koyi kyawawan dabi’u na kyautatawa da soyayya da kuma hakuri da juna kamar yadda Annabinmu Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi misali da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...