NNPC ta bayyana Dalilin da Yasa Farashin Fashin Man Fetur ya kai N617/Lita

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban rukunin kamfanin man fetur na Najeriya NNPC , Mele Kyari, ya ce yanayin kasuwar man fetur ce tasa farashin man ya kai Naira 617.

 

Kyari ya bayyana haka ne a yammacin ranar Talata bayan ganawarsa da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Talla

Ya ce idan aka karkata akalar man fetur, hakikanin kasuwa zai sa farashin man fetur ya tashi a wasu lokutan, wani lokacin kuma yasa ya sauka.

Shekarar musulunci: Gwamnatin Kano ta bada hutu ga ma’aikata

Shugaban na NNPC, ya ce karin farashin man na kowace litar daga sama da N500 zuwa N617 ba batun karancin sa ba ne, yana mai tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa Nigeria na da wadataccen man kasa.

Kyari ya ce Najeriya na da wadataccen man da za’a iya yin kwanaki 32 amfani da shi ba tare da an sami karancin sa ba.

Kyari ya ce tawagar harkokin kasuwanci ta NNPCPL ce ke da alhakin daidaita farashin kuma ayarin zai “daidaita farashin daidai da yanayin da kasuwa ta nuna ”.

Ya ce, “Hakika abin da ke faruwa ke nan; wannan yana tabbatar da cewa kasuwa ta daidaita kanta ta yadda farashin zai tashi, wani lokacin ma yakan sauko”.

Kyari ya tabbatar wa ‘yan Nigeria cewa tashin farashin man fetur din ba shi da alaka da matsalar samar da man.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...