Cikin shekaru uku Mutane miliyan 165 sun faɗa ƙangin talauci – Majalisar Dinkin Duniya

Date:

 

Majalisar Dinkin Duniya ta ce an samu ƙaruwar talauci a matalautan kasashe, inda adadin mutanen da ke rayuwa ƙasa da dala 3.65 a shekarar 2023 ya kai miliyan 165.

 

Rahoton ya ambato shugaban Hukumar UNDP Achim Steiner ya ce ”Kasashen da suka zuba jari cikin shekaru uku da suka gabata, domin tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi, sun taimaka wajen kare al’ummarsu da dama daga faɗawa ƙangin na talauci.

Talla

 

BBC Hausa ta rawaito Cikin wani rahoton da Hukumar Raya Ƙasashe Ta Majalisar Dinkin Duniya UNDP ta fitar ranar Alhamis, ya ce annobar Korona da hauhawar farashi da kuma yaƘin Ukraine sun tilasta wa mutum miliyan 165 shiga Ƙangin talauci tun shekarar 2020 zuwa 2023.

Yanzu-Yanzu: Yadda Tinubu zai samar da hukumar kula da farashin abinci a Nigeria

A yayin da ya ce ƙasashen da ba su yi wani hoɓɓasa wajen rage talaucin suka fi fuskantar matalar ƙaruwar matalauta a cikin al’ummominsu.

Majalisar Dinkin Duniyar ta kuma yi kiran a sassauta wa ƙasashe masu tasowa biyan bashi.

”A yau ƙasashe 46 na kashe fiye da kashi 10 na kuɗin shigar da suke samu wajen tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi a ƙasashen”, in ji shi.

A cewar rahoton biyan bashi da ƙasashen ke yi na ƙara musu wahalhalu wajen tallafa wa talakawan cikinsu a bangarorin lafiya da ilimi da sauran bukatun rayuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...