Yanzu-Yanzu: Tinubu ya nemi Majalisar Wakilai ta sahale ya kashe Naira Biliyan 500 don Tallafawa Yan Nigeria

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Shugaban kasar Nigeria, Bola Ahmed Tinubu ya rubutawa majalisar wakilai wasika, yana neman a yi masa gyara a kwarya-kwaryar kasafin kudin shekarar 2022 domin daukar Naira biliyan 500 domin samar da tallafi ga al’ummar Nigeria.

A ranar Laraba, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas ya karanta wasikar shugaban a zauren majalisar.

Talla

Abbas ya ce bukatar ta zama dole domin baiwa gwamnati damar samar da tallafi ga ‘yan Najeriya domin dakile radadin cire tallafin man fetur.

Shari’ar zaɓen gwamnan Kano: INEC ta gabatar da na’urar BVAS 21 ga kotu

“Na rubuta wannan wasika ne domin neman a gyara dokar karin kasafin kudin na shekarar 2022. Bukatar ta zama dole a wannan lokaci don samar da kudaden da za’a samar da abubuwan da suka dace don rage radadin cire tallafin man fetur ga ‘yan Najeriya.

“Don haka, an ciro Naira biliyan 500 kawai daga cikin karin kasafin kudi na shekarar 2022 na Naira biliyan 819, 536, 937, 937, 803 kawai don samar da kayan agaji ga ‘yan Najeriya don magance wahalhalun da yan Nigeria suke fuskanta sakamakon cire tallafin,” in ji wasikar.

Ya bukaci yan majalisar da su gaggauta Amincewa da bukatar don baiwa gwamnatinsa damar samar da abubuwan jin kai ga ‘yan Najeriya.

Bayan karanta wannan bukata, kakakin majalisar ya ce majalisar za ta fara nazarin bukatar shugaban a ranar Alhamis.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...