Tsaftar Muhalli: Zamu haɗa kai da shugabannin kasuwani a kano – Amadu Danzago

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago ya bayyana bukatar dake akwai na samar da wani tsari tsakanin hukumar sa da shugabannin kasuwannin jihar nan a bangaren tsaftace kasuwannin.

Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a kasuwar kantin kwari, lokacin da ake gudanar da aikin kwashe sharar Wanda shine Karo na 4 a kasa da makwanni 2.

Talla

Dan zago yace hukumarsa da gwamnati ba za su cigaba da zura idanu da yawa daga cikin kasuwannin jihar nan suna cigaba da rufe tituna sanadin sharar da suke zubarwa a akan titunan ba.

Jerin sunayen ministoci: Shugaban APC, Adamu ya bayyana dalilin da ya sa Tinubu ya yi jinkiri fitar da ministoci

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar ta kwari sun bayyana cewa ana fito da sharar ne daga cikin kasuwar a tsakiyar dare da Kuma unguwar fagge ta yadda sai dai su wayi gari suga sharar ta toshe hanyar wucewa.

Dan zago yace duba da yadda gwamnati take kashe makudan kudade wajen aikin kwashe sharar akwai bukatar al’umma su bada cikakken hadin Kai da goyon baya domin samun nasarar da aka Sanya a gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...