NEMA ta buƙaci gwamnoni su zauna cikin shiri kan yiwuwar samun ambaliya

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Nigeria NEMA, Ahmed Habib ya shawarci gwamnonin Kasar da su samar da cibiyoyin bayar da agajin gaggawa a jihohinsu domin kare afkuwar ambaliya.

 

“Idan gwamnonin za su bai wa hukumar haɗin-kai da kuma karɓar shawara, to ba za a iya rage asarar da aka samu a bara”.

Talla

Shugaban Hukumar ya bayyana haka ne bayan wani zama da ya yi da wasu gwamnoni a Abuja, babban birnin Nigeria.

Mun tantance mutane 800 cikin 1200 da suka nemi shiga shirin tura ɗalibai kasashen waje – Gwamnatin Kano

Ya kuma bukaci gwamnonin da su wayar da kan mutane kan muhimmancin komawa yankunan da ba su da haɗarin fuskantar ambaliya domin kare asarar rayuka da kuma dukiyoyi da sauransu.

Habib ya kuma ce akwai bukatar a taimakawa hukumar da kuɗaɗe saboda hakan zai taimaka wajen kare afkuwar bala’o’i da za a iya samu.

A makon da ya gabata ne, NEMA ta yi hasashen cewa za a iya samun ambaliya a jihohi14 na faɗin Najeriya sakamakon mamakon ruwan sama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...