Kungiyar KEBBI DALA FARMERS ta tallafawa manoman arewacin Nigeria

Date:

Daga Abdulbaki Ali Sharifai

 

Kungiyar Kebbi Dala Farmers, ta tallafawa manoman da suka fito daga yankin Arewacin Najeriya da kayan noma da wayoyin hannu da za su yi amfani dasu domin kara samun ilimi a bangaren aikin noma.

Kungiyar ta Dala Kebbi Farmers dake da rassa a jihohi 17 na Arewacin Najeriya, nada manufar ingantawa da saukakawa manoma samun kayan aikin gona kamar iri da takin zamani acikin farashi mai sauki.

Talla

Acewar shugaban kungiyar Comrade Habib S Umar, an samar da kungiyar ne domin saukakawa manoma,” an samar da wannan kungiya domin baiwa manoma horo da kuma samar musu da kayan noma cikin farashi mai sauki” inji Comrade Habib.

Yanzu-Yanzu: Shugaba Tinubu Ya Zama Shugaban ECOWAS

Comrade Habib yacigaba da cewa” Muna basu damar ajiye kayan amfanin gonarsu har lokacin da kayan noman zasuyi darajar da zasu maida abinda suka kashe”.

“Kuma idan mun basu bashi suna biyanmu ne da kayan noma, ragowar kuma sunada damar siyar mana ko su saidawa wasu, ko kuma mu ajiye musu” Comrade Habib S Umar.

Kungiyar dai tayi hadin gwiwa ne da Kamfanin Kingo Mobile domin baiwa manoman bashin wayar hannu cikin farashi mai sauki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...