Gwamnatin Sokoto ta kafa kwamiti don binkicen gwamnatin Tambuwal

Date:

Gwamnatin jihar Sokoto ta kafa wani kwamiti da zai bincike kan batun mallakar filaye da yadda aka sayar ko a ka yi gwamjon kadadrorin gwamnati a zamanin mulkin tsohon gwamnan jihar Sanata Aminu waziri Tambuwal.

 

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar Abubakar Bawa ya fitar, ya ce kwamitin mai mutane biyar ƙarƙashin jagorancin Justice M.A. Pindiga zai kuma duba asusun gwamnatin jihar domin gano adadin kuɗaɗen da aka samu sakamakon sayar da kadarorin.

Talla

BBC Hausa ta rawaito Sanarwar ta kara da cewa kwamitin zai kuma duba batun filayen da sabuwar gwamnatin ta ke zargin gwamnatin da ta shuɗen ta rabar ciki har da gidajen gwamnatin jihar da aka yi yi gwanjonsu.

Da dumi-dumi: Kamfanin KEDCO ya bayyana dalilin da yasa za’a rasa wuta a Kano

Haka kuma akwai batun motocin gwamnatin jihar da na kananan hukumomi.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗar da Barrister Nasiru Muhammed Binji a matsayin sakatare, sai Chief Jacob E. Ochidi, SAN, da Alhaji Usman Abubakar da kuma Barrister Lema Sambo Wali a matsayin mambobi.

An bai wa kwamitin watanni biyu domin gabatar da rahoton sakamkon bicikensa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...