FERMA ta fara gyaran wasu tituna a faɗin Nijeriya saboda Damina

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Hukumar kula da tituna ta ƙasa wato FERMA, ta ce ta fara shirin cike ramuka tare da gyaran hanyoyin da suka lalace a fadin kasar nan yayin da damina ta shigo.

 

“Ya zama wajibi a dauki matakin ne saboda bukatar da ake da ita na rage wahalhalu da tsaikon da direbobi ke fuskanta a tituna a kullum a fadin Nigeria.

Talla

Manajan-Darakta na riƙo na hukumar ta FERMA, Godson Amos ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa a yau Lahadi a Abuja.

Ya kamata ayi dokar da zata hana karya ka’idojin Hausa a allunan tallace – tallace  Dr. Saifullahi Dahiru

Ya bayyana kwarin gwiwa cewa za a samu nasarar aikin a cikin makwanni shida, kuma za a yi aiki cike da dukkanin ramuka da gyara lalacewar hanyoyi, kan manyan tituna a fadin kasar.

Ya ce ya samu rahotanni a fadin kasar nan na lalacewar manyan tituna da ke fadin kasar, wanda a cewar sa, ya jawo wa masu amfani da hanyoyin matsala.

Ya kara da cewa lalacewar na kawo cikas ga harkokin tattalin arziki saboda yadda jama’a ba su iya kwashe kayayyaki daga wannan wuri zuwa wancan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...