Daga Maryam Muhammad Ibrahim
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umurnin rage yawan ma’aikatun jihar daga 28 zuwa 16.
Lawal ya ce an dauki matakin ne don sauya fasalin ma’aikatun gwamnati don samar da ayyuka masu inganci a jihar.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan a sashihin shafin sa Facebook a ranar Alhamis, ya kara da cewa sake fasalin gwamnatin jihar ya yi daidai da manufarsa ta samar da majalisar zartarwar mai inganci da za ta rage kashe kudaden gwamnati don wadata al’ummar Zamfara da aiyukan cigaba.
Bidiyon Dala: Ganduje ya Magantu kan Gayyatar da Muhuyi Magaji Rimin Gado ya yi masa
Ya rubuta: “A wani bangare na yunkurin gwamnatina na sauya fasalin ma’aikatun gwamnati don samar da ingantacciyar rayuwa ga al’ummar mu ta hanyar rage kashe kudaden gwamnati, na ba da umarnin sake fasalin da rage yawan ma’aikatunmu daga 28 zuwa 16.
“An yi hakan ne bisa kudirina na samun majalisar zartarwar mai inganci wacce za ta rage tsadar harkokin mulki tare da samar wa jama’armu aiyukan raya kasa da ci gaban al’umma”