Hajjin bana: Alhazan Najeriya 13 ne suka rasu a kasar Saudiyya

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Hukumar kula da aikin hajji ta Nigeria NAHCON, ta bayyana cewa Alhazan Najeriya da suka mutu a aikin hajjin bana sun kai 13, kuma wasu 41,632 suka kamu da rashin lafiya a kasar Saudiyya.

 

Shugaban tawagar likitocin Najeriya mai kula da alhazan ƙasar, Dr Usman Galadima ne ya bayyana hakan a daren Lahadi a birnin Makkah yayin taron bibiyar yadda al’amura ke tafiya bayan Arafat.

Talla

A jawabinsa, Dr Galadima ya bayyana cewa, jimillar mahajjata bakwai ne suka rasu kafin Misha’ir – tafiya daga Mina zuwa Arafat, da komawa Mina – yayin da wasu shida kuma suka rasu a lokacin Misha’ir.

Sallah: Gwamnan Kano ya nemi afuwar Sarkin Gaya kan abun da ya faru a gidan gwamnati yau

Ya ba da shawarar a riƙa yi wa maniyyata cikakken gwajin lafiya kafin tafiya aikin Hajji tare da ba da takardar shaidar cewa suna cikin ƙoshin lafiya.

NAHCON ta ayyana ranar da za’a fara dawo da Alhazan Nigeria gida

Ya ce kamata ya yi a hana tsofaffin alhazai da majinyata marasa lafiya daga zuwa Jamarat (wurin da alhazai ke jifan shaidan).

Ya kuma buƙaci a riƙa aiwatar da hada-hadar mahajjata kamar yadda hukumomin Saudiyya suka ba da shawara.

Jaridar Daily trust ta rawaito a buƙaci jihohin da ke da motocin ɗaukar marasa lafiya su gabatar da su don aiki tare da jami’an likitocin kula da mahajjata na ƙasa don samun ƙarin haɗin kai a kan lamuran da ke buƙatar gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...